Kano Times

July 13, 2025

Babban Bankin Najeriya ya bayar da tabbacin wadatuwar takardun kuɗi

Babban bankin Najeriya ya sanar da ‘yan Najeriya tabbacin ba wata matsalar ƙarancin takardun kuɗi da za a fuskanta a ƙasar.

Hakan dai na zuwa ne yanda aka wayi gari a satin da suka wuce ana fuskantar ƙarancin ƙudi a wasu sassan na wasu manyan biranen Nijeriyar. Wuraren da kuɗaɗen suka fi karanci akwai injin cirar kuɗi na banki, sai masu wajen cirar kuɗi a shaguna da kuma wurin ‘yan canji.

A sanarwar da daraktan sadarwa na babban bankin ƙasar ya sakawa hannu, Isa AbdulMumin, ya bayyana cewar a binciken da suka yi sun gano yanda bankunan kasuwa suka kwashi kuɗaɗe masu yawa ne a manyan biranen ƙasar da har jama’a suka fara shiga matsi na ƙarancin takardun kuɗin idan sun je cira a banki ko shaguna.


Ya ƙara da cewar akwai takardun kuɗaɗe masu yawa da za su wadata a ƙasa baki ɗaya. Don haka fargaba da zullumin ba su da wani alfanu.

Leave a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Scroll to Top