HomeHausaAtiku ya buƙaci Kwankwaso da Peter Obi su haɗa hannu da shi...

Atiku ya buƙaci Kwankwaso da Peter Obi su haɗa hannu da shi wajen binciken Tinubu

Ɗan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaɓen Najeriya na 2023, Atiku Abubakar, ya bukaci sauran ƴan takara na hamayya, Peter Obi da Rabi’u Musa Kwankwaso su haɗa ƙarfi da shi a ƙoƙarinsa na bincike kan takardun karatun shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.

Atiku ya bayyana hakan ne a wani taron manema labarai da ya gudanar a Abuja a yau ranar Alhamis.

Ya ce abin da yake fafutuka a kai shi ne tabbatar da bin diddigi domin yin adalci da kuma gaskiya a Najeriya.

Atiku dai ya shigar da ƙara kan shugaban kasa Bola Tinubu game da takardunsa na karatu a jami’ar jihar Chicago.

Ya bukaci samun takardun ne domin su zama shaida ga zarginsa na jabun satifiket din Tinubu na CSU.

spot_img
spot_img
spot_img
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

- Advertisment -

Most Popular

Recent Comments