Kano Times

July 9, 2025

An Naɗa Amina J. Mohammed Sarauniyar Wajen Gombe

Masarautar Gombe da ke Arewa maso gabashin Najeriya ta naɗa mataimakiyar Sakare Janar na Majlisar Dinkin Duniya, Amina J Mohammed, sarautar Sarauniyar Wajen Gombe.

Mai martaba Sarkin Alhaji Abubakar Shehu Abubakar lll ne ya tabbatar da haka a cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook a yau juma’a

Mai Martaba Sarkin Gombe Alh. (Dr) Abubakar Shehu Abubakar lll, CFR. Ya tabbatarwa Hajiya Dr. Amina J. Mohammed sarautar (Sarauniyar Wajen Gombe).

Hajiya Amina J Mohammad :- Tsohuwar ministan muhalli na tarayyar Najeriya kuma mataimakiyar Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya dake New York a kasar Amurka”

Amina Mohammed ta fara shiga Majalisar Dinkin Duniya ne a shekarar 2012 a matsayin mai baiwa Ban Ki-moon tsohon babban sakataren Manofofin Ci Gaban Karni Na Majalisar Dinki Duniya (MDD) shawara Ta musamman da alhakin tsare-tsaren ci gaba.

Leave a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Scroll to Top