Kano Times

November 11, 2025

Sarkin Ƙasar Ebira, Ohinoyi Ya Rasu

Allah Ya yi wa Mai Martaba Sarkin Kasar Ebira, Ohinoyi Abdul Rahman Ado Ibrahim (CON) rasuwa.

Mai Martaba Abdul Rahman Ado Ibrahim, ya rasu ne a fadarsa da ke garin Okene a Jihar Kogi kafin wayewar garin Lahadi.

Ya koma ga Mahaliccinsa ne yana da shekaru 94 a duniya, kuma bayan shekaru 25 a karagar mulkin Masarautar Kasar Ebira da ke Jihar Kogi.

Ya hau mulki ne a shekarar 1997 bayan rasuwar Ohinoyi Sanni Omolori.

Leave a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Scroll to Top